Connect with us

News

An damƙe kwamandan vigilante kan zargin ganawa ƴar sanda azaba a Anambra

Published

on

FB IMG 16423316688593920
Spread the love

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

Advertisement

Kwamishinan Ƴan Sanda na Jihar Anambra, Echeng Echeng ya ce rundunar sa ta cafke kwamandan ƴan vigilante na jihar a kan zargin ganawa wata ƴar sanda azaba.

An cafke kwamandan ne, wanda a ka sakaya sunansa, bayan da ya azabtar da ƴar sanadan a Ƙaramar Hukumar Awuda Nnobi in Idemili ta Kudu a ranar 12 ga watan Janairu.

Kakakin Rundunar a jihar, Tochukwu Ikenga, a wata sanarwa da ya fitar, ya sanar da cewa kwamandan na hannun ƴan sanda a tsare.

Advertisement

Ikenga ya yi bayanin cewa wani fefen bidiyo da ya yi ta yawo a yanar gizo, inda a ka nuna jami’an vigilante ɗin su na azabtar da ƴar sandar a ofishin su ne ya sanya Kwamishinan Ƴan Sandan jihar ya bada umarnin a kamo kwamandan.

Kwamishinan ya kuma bada umarnin bincike a kan lamarin.

“Rundunar ta suffanta lamarin a matsayin tsoro, inda ya ƙara da cewa rundunar a shirye ta ke da ta kare mata wajen cin zarafi da a ke yi musu, ko da ma ba jami’ar tsaro ba ce,”

Advertisement

Kakakin ya kuma godewa al’umma sakamakon alla-wadai da su ka yi da abin da ya faru.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *