Connect with us

News

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da shirinta na janye tallafin man fetur

Published

on

FB IMG 16422460817653375
Spread the love

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta dakatar da shirinta na janye tallafin man fetur har sai baba ta gani.

A baya dai gwamnatin ta shirya janye biyan kuɗaɗen tallafin man fetur ɗin a watan Yulin shekarar nan ta 2022.

Ministar kuɗi da kasafi da tsare-tsare ta Najeriya Zainab Ahmed ce ta sanar da hakan a wani taro da aka yi a majalisar dokoki a yau Litinin a Abuja.

Advertisement

Taron ya samu halartar shugaban majalisar dattawa Ahmed Lawan da ƙaramin ministan man fetur Timipre Sylva, da kuma shugaban kamfanin mai na NNPC Mele Kyari.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *