Connect with us

News

Boko Haram Ta Sake Kai Hari Kan Sansanoni Biyu Na Soji A Borno

Published

on

FB IMG 1747131555800
Spread the love

Wasu mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare kan sansanonin sojojin Najeriya guda biyu da ke Jihar Borno, inda suka kashe wasu sojoji, kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

Mayaƙan sun kai hare-haren ne a sansanonin soji da ke yankunan Kale-Balge da Gajiram da ke jihar. Har zuwa yanzu, ba a fitar da cikakken bayani ba kan adadin sojojin da suka rasa rayukansu ko irin barnar da aka yi.

Majalisar Kano Ta Amince Da Kafa Hukumar Hukunta Masu Karya Dokar Hanya

FRI HAUSA ta ruwaito cewa  an ji karar harbe-harbe na tsawon lokaci, lamarin da ya jefa jama’a cikin fargaba, inda da dama suka gudu daga gidajensu.

Wannan hari na zuwa ne kasa da awanni 24 bayan wani makamancin sa da aka kai wa sojoji a garin Marte, wanda ke a yankin Arewa maso Gabashin jihar.

Advertisement

Hukumomin tsaro dai ba su ce komai ba tukuna kan harin.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *