News
Kotu Ta Tsare Matar Aure Bisa Zargin Kashe Jaririn Mijinta A Kano
Wata kotun majistare da ke zamanta a Kano ta umarci a tsare wata matar aure, Zayya Magaji, bisa zargin kashe ƙaramin ɗan mijinta ta hanyar ba shi guba.
Ana zargin matar, mazauniyar ƙauyen Danbango a ƙaramar hukumar Kabo ta Jihar Kano, da haddasa mutuwar yaron mijinta mai shekara uku.
Gwamnatin Filato Ta Sassauta Dokar Hana Fita A Jos
Lauyan gwamnati, Barrista Muhammad Aliyu, ne ya gurfanar da ita a gaban kotu, inda magatakardar kotu, Nafiu Sani, ya karanta mata tuhume-tuhumen da ake yi mata.
A cewar masu gabatar da ƙara, matar ta aikata laifin ne ta hanyar ba yaron guba, wanda hakan ya janyo mutuwarsa.
Sai dai wadda ake tuhuma ta musanta zargin, tana mai cewa ba ta aikata laifin da ake zarginta da shi ba.
Lauyan gwamnati ya kuma bayyana wa kotu cewa an tura takardun shari’ar zuwa Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano domin samun shawarar doka kafin ci gaba da shari’ar.
Alƙalin kotun, Mai Shari’a Auwal Yusuf, ya amince da buƙatar dage shari’ar, tare da bayar da umarnin a tsare wadda ake zargin a gidan yari.
Kotun ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 29 ga watan Afrilu, domin ci gaba da shari’ar.
