News
Dakarun Sojin Sun Kwato Dabbobi 529 Daga Hannun Barayin Daji A Katsina
Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce dakarunta na Forward Operation Base (FOB) Malumfashi da ke aikin wanzar da tsaro a Jihar Katsina sun ƙwato dabbobi 529 daga hannun ɓarayin daji bayan sun yi fafatawa mai zafi da ‘yanta’addan.
Wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Lahadi ta ce dakarunta, waɗanda Laftanar Kanar MM Isa, ya jagoranta bayan sun samu bayanan sirri game da ɓarayin dajin, sun yi musu kwanton-ɓauna a yankin Kasuwan Sabo na ƙaramar hukumar Kafur ranar 7 ga watan Fabrairun 2026.
Gwamnan Abia Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tallafin Tsofaffi
Ta ƙara da cewa ɓarayin dajin sun shiga Katsina ne daga Jihar Zamfara kuma Idi Abasu Aiki, ɗan’uwan gawutaccen ɗan fashin dajin nan Ado Aliero, shi ne ya shugabance su.
Bayan sojojin Nijeriya sun ci ƙarfin ‘yan fashin dajin, sun ƙwato dabbobi 529 da suka haɗa da shanu 290, da tumaki 238 da jaki ɗaya da kuma babur guda ɗaya, in ji sanarwar. Sanarwar ta ce babu wani sojan Nijeriya da ya mutu ko ya jikkata.
