Politics
Zaɓen 2027: Matashin dan jarida Ya amsa kiran al’ uammar Akko ta Arewa
Dan jarida Usman Abubakar Usmaniyya, ya sanar da a niyyarsa ta tsayawa takarar ɗan Majalisar Dokokin Jihar Gombe a zaɓen shekarar 2027, bayan abin da ya bayyana a matsayin kiraye-kirayen da al’ummar yankin ke yi masa.
A wata sanarwa da ya fitar, Usmaniyya ya ce ya yanke wannan shawara ne bisa kishin al’umma da ƙudurinsa na wakiltar muradun jama’a cikin gaskiya, tare da kare haƙƙoƙinsu da kuma tabbatar da cigaba mai ɗorewa.
Yadda Cacar Zamani Ke Lalata Rayuwar Matasan Arewacin Nijeriya
Ya bayyana cewa yana da yakinin cewa haɗin kai, addu’a da goyon bayan al’umma za su taimaka wajen samar da wakilci nagari a Akko ta Arewa.
Usman Abubakar Usmaniyya ya kuma miƙa kansa ga al’ummar yankin domin neman cikakken goyon bayansu, yana mai addu’ar Allah Ya sanya wannan takara ta zama alkhairi ga yankin baki ɗaya.
Sanarwar ta samu sa hannun Magatakarda, Alamin Sirajo Bappah, Usman Abubakar Usmaniyya (Tauraron Gona)
-
News4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News2 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
