News
NSCDC Ta Hukunta Jami’ai 79 Tare Da Sallamar 37 Kan Zargin Rashawa Da Sata
Hukumar tsaro da kare fararen hula ta Najeriya (NSCDC) ta sanar da hukunta jami’anta 79 saboda laifuffuka daban-daban da suka haɗa da cin hanci, damfarar aikin yi, sata, sakaci, da karya ƙa’idojin aiki.
Daga cikin jami’ai 37 da aka sallame su daga aiki, yayin da wasu ke fuskantar shari’a da hukuncin ritaya ta dole.
Bayan Watanni Shida, An Ceto Mutane 176 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kwara
Babban kwamandan NSCDC, dakta Ahmed Audi, ya ce cikin waɗanda aka sallama akwai jami’ai biyu na rundunar Mining Marshals da aka samu da laifin gudanar da aiki ba tare da izini ba, lamarin da ya haddasa mutuwar kwamandansu a Jihar Nasarawa.
Hakazalika hukumar ta kama mutum 18 da ake zargi da lalata bututun mai, satar kayan layin dogo, lalata kayayyakin wutar lantarki da kuma safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai wanda aka tare a Enugu da makaman soja, alburusai da wasu kayayyakin da ake zargin na haɗa bama-bamai ne.
NSCDC ta ce za ta ci gaba da ɗaukar mataki kan duk wani jami’i ko farar hula da aka samu da laifi, tare da kira ga ‘yan Najeriya su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanan sirri domin kare muhimman kadarorin ƙasa.
-
News4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
-
News1 day ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
