Entertainment
“Idan Aka Yi Maguɗi A Zaɓen Gwamnan Jihar Osun, Zan Kai Ƙorafi Wajen Trump” – Davido
Fitaccen mawaƙin Najeriya, David Adeleke (Davido), ya yi gargaɗin cewa zai kai ƙorafi ga Shugaban Amurka, Donald Trump, idan aka samu maguɗi ko wata rashin gaskiya a zaɓen gwamnan jihar Osun mai zuwa.
Davido ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa kai tsaye a shafukan sada zumunta, inda ya ce ba zai amince da duk wani yunƙuri na karkatar da sakamakon zaɓe ba.
Gwamna Yusuf ya jagoranci daurin auren gata na zawarawa da ’yan mata 1,500 a Kano
Ya kuma yi kira ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki da su tabbatar da cewa an gudanar da zaɓen cikin lumana, gaskiya da adalci domin kare martabar dimokuraɗiyyar Najeriya.
Kalaman na Davido sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda mutane ke ci gaba da bayyana ra’ayoyinsu kan batun yayin da ake tunkarar zaɓen gwamnan jihar Osun.
-
News6 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News6 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
