Politics
2027: Gashash Ya Gabatar Da Tsarin Ci Gaban Kano Bisa Bukatun Jama’a
Ɗan takarar gwamnan Jihar Kano na Jam’iyyar Accord a zaɓen 2027, Ambasada Dakta Mukhtar Gashash, ya bayyana wani sabon tsarin tafiyar da mulki da ya ce zai bai wa al’ummar jihar damar taka rawa kai tsaye wajen tsara manufofin gwamnati da abubuwan da suka fi muhimmanci ga ci gaban yankunansu.
Gashash ya bayyana shirin ne a ƙarƙashin taken “Tsarin Jama’a na Samar da Ingantacciyar Kano”, inda ya ce idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta sauya salon mulkin da ake tsara manufofi daga sama zuwa ƙasa, tare da mayar da hankali kan sauraron jama’a da kuma aiki tare da su.
An Daure Matashi Shekaru 10 Bayan Amfani Da ChatGPT Wajen Shirya Fashin Banki
A cewarsa, kowace Ƙaramar Hukuma a jihar za ta samu damar tsara nata tsarin ci gaba bisa buƙatu da matsalolin da mazauna yankin ke fuskanta.
Ya ce manoma, ’yan kasuwa, mata, matasa, malamai, ƙwararru, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki za su shiga cikin tsarin domin gano matsalolin al’umma da kuma samar da hanyoyin magance su.
“Ba zan yi mulkin Kano saboda jama’a ba, zan yi mulkin Kano tare da jama’a,” in ji Gashash.
Ya ƙara da cewa ba zai yiwu mutum ɗaya ya fahimci dukkan ƙalubalen da al’ummomi daban-daban ke fuskanta ba tare da sauraron mutanen da matsalolin suka shafa ba.
“Jama’a sun san matsalolinsu, sun san irin wahalhalun da suke fuskanta, don haka dole ne su samu damar bayyana ra’ayoyinsu wajen tsara makomarsu,” ya ce.
Gashash ya kuma yi alkawarin samar da gwamnati mai sauƙin samun damar tuntuɓarta, inda ya ce gwamnatinsa za ta ƙarfafa jama’a su gabatar da koke-koke, shawarwari da ra’ayoyinsu ba tare da tsoro ba.
Ya bayyana gwamnati a matsayin “gidan jama’a”, inda kowane ɗan ƙasa zai samu damar a saurare shi da kuma mutunta shi ba tare da la’akari da matsayinsa na zamantakewa ko tattalin arzikinsa ba.
Ɗan takarar na Accord ya ce tuntubar jama’a, riƙon amana, haɗa kai da kuma bai wa kowa dama za su kasance cikin muhimman ginshiƙan gwamnatinsa.
“Ba zan zo gwamnati da tunanin cewa ni ne na san komai ba. Zan zo ne a shirye nake in saurara, in koya, in yi wa jama’a hidima, sannan in yi aiki tare da ku,” in ji shi.
Ya ce al’ummomi za su shiga cikin gano matsalolinsu, tsara hanyoyin magance su, ayyana abubuwan da suka fi muhimmanci da kuma sanya ido kan yadda ake aiwatar da shirye-shiryen gwamnati.
Gashash ya jaddada cewa burinsa ba wai kawai gina ababen more rayuwa ba ne, sai dai kuma gina al’ummomi masu ƙarfi da za su iya taka rawa wajen tafiyar da harkokin jihar.
“Ina son in bar baya ba ayyuka kawai ba, har da al’umma da za ta iya cewa: ‘An saurare mu, mun shiga cikin harkokin gwamnati, mun taimaka wajen gina wannan Kano,’” ya ce.
Ya kuma yi kira ga al’ummar Kano da su yi amfani da zaɓen 2027 wajen zaɓar irin gwamnatin da suke so, tare da taka rawa wajen tsara makomar jihar.
“Kano tamu ce baki ɗaya. Makomarta tamu ce baki ɗaya. Kuma tare za mu gina ta,” in ji shi.
Gashash ya kammala da bayyana taken kamfen ɗinsa da cewa: “Idan mafi rauni ya yi murmushi, Kano ta yi nasara.”
-
Uncategorized6 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News20 hours ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
