News
EFCC Ta Dakatar Da Asusun Gwamnatin Osun Ne Kan Zargin Almundahanar Miliyoyin Naira
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya, EFCC, ta ce ta dakatar da asusun gwamnatin jihar Osun bisa zargin yadda aka tafiyar da wasu kuɗaɗen tallafi da na ayyukan muhalli da suka kai naira biliyan 11.
Hukumar ta ce ta fara binciken gwamnatin jihar tun watan Maris, inda ta ce wasu manyan jami’ai ciki har da babban akanta na jihar sun gurfana a gabanta.
WASSCE 2026: Kashi 61.5 Cikin 100 Na Ɗalibai Sun Samu Darussa Biyar Har Da Turanci Da Lissafi
EFCC ta bayyana cewa ta ɗauki matakin ne bayan ta gano wasu manyan kuɗaɗe na fita daga asusun zuwa wasu kamfanoni.
Sai dai gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya ce ba za su amince da abin da ya kira take haƙƙin jiha ba, yana mai cewa zai ƙalubalanci matakin a kotu.
-
News4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
-
News1 day ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
