News
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
Hedkwatar rundunar “Operation Haɗin Kai” a Nijeriya ta ce wasu mutane shida da ake zargi mayakan ISWAP ne, tare da iyalansu, sun miƙa wuya ga dakarun bataliya ta 192.
Muƙaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Rundunar Soji, na Hedkwatar Haɗin Gwiwa ta Shiyyar Arewa Maso Gabas (Operation Haɗin Kai) da ke Maiduguri, Kyaftin Mohammed Goni ne ya bayyana haka a wata sanarwa a ranar Laraba.
Yan Bindiga Sun Sace Daliban Jami’ar Gwamnatin Tarayya A Nasarawa
Sanarwar ta ƙara da cewa dakarun bataliya ta 115, yayin da suke gudanar da ayyukan bincike da ceto a yankin ƙaramar hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno a ranar 7 ga watan Yuli, sun ceto ƙarin mutane biyu da aka sace a maɓoyar ’yanta’adda.
Ta ce za a ci gaba da gudanar da ayyukan bincike da kuɓutar da mutane ba tare da gajiyawa ba, har sai an gano kowane mutum da aka sace kuma an mayar da shi ga iyalansa cikin ƙoshin lafiya.
Abubuwan da aka ƙwato a hannun ’yanta’addan da iyalansu sun haɗa da jimillar kuɗi sama da Naira miliyan 1.5, wayoyin salula na Tecno guda biyu, da sauran kayayyaki.
-
Uncategorized4 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
-
News2 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
