News
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
Hedkwatar rundunar “Operation Haɗin Kai” a Nijeriya ta ce wasu mutane shida da ake zargi mayakan ISWAP ne, tare da iyalansu, sun miƙa wuya ga dakarun bataliya ta 192.
Muƙaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Rundunar Soji, na Hedkwatar Haɗin Gwiwa ta Shiyyar Arewa Maso Gabas (Operation Haɗin Kai) da ke Maiduguri, Kyaftin Mohammed Goni ne ya bayyana haka a wata sanarwa a ranar Laraba.
Yan Bindiga Sun Sace Daliban Jami’ar Gwamnatin Tarayya A Nasarawa
Sanarwar ta ƙara da cewa dakarun bataliya ta 115, yayin da suke gudanar da ayyukan bincike da ceto a yankin ƙaramar hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno a ranar 7 ga watan Yuli, sun ceto ƙarin mutane biyu da aka sace a maɓoyar ’yanta’adda.
Ta ce za a ci gaba da gudanar da ayyukan bincike da kuɓutar da mutane ba tare da gajiyawa ba, har sai an gano kowane mutum da aka sace kuma an mayar da shi ga iyalansa cikin ƙoshin lafiya.
Abubuwan da aka ƙwato a hannun ’yanta’addan da iyalansu sun haɗa da jimillar kuɗi sama da Naira miliyan 1.5, wayoyin salula na Tecno guda biyu, da sauran kayayyaki.
-
News2 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News3 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News3 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
