Connect with us

News

Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji 

Published

on

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 101 Sun Kama Wasu 182 A Cikin Mako Daya
Dakarun Sojin Najeriya

Hedkwatar rundunar “Operation Haɗin Kai” a Nijeriya ta ce wasu mutane shida da ake zargi mayakan ISWAP ne, tare da iyalansu, sun miƙa wuya ga dakarun bataliya ta 192.

Muƙaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Rundunar Soji, na Hedkwatar Haɗin Gwiwa ta Shiyyar Arewa Maso Gabas (Operation Haɗin Kai) da ke Maiduguri, Kyaftin Mohammed Goni ne ya bayyana haka a wata sanarwa a ranar Laraba.

Yan Bindiga Sun Sace Daliban Jami’ar Gwamnatin Tarayya A Nasarawa

Sanarwar ta ƙara da cewa dakarun bataliya ta 115, yayin da suke gudanar da ayyukan bincike da ceto a yankin ƙaramar hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno a ranar 7 ga watan Yuli, sun ceto ƙarin mutane biyu da aka sace a maɓoyar ’yanta’adda.

Ta ce za a ci gaba da gudanar da ayyukan bincike da kuɓutar da mutane ba tare da gajiyawa ba, har sai an gano kowane mutum da aka sace kuma an mayar da shi ga iyalansa cikin ƙoshin lafiya.

Abubuwan da aka ƙwato a hannun ’yanta’addan da iyalansu sun haɗa da jimillar kuɗi sama da Naira miliyan 1.5, wayoyin salula na Tecno guda biyu, da sauran kayayyaki.

Advertisement

 

 

TRT AFRIKA 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending