News
Dakarun Soji Sun Dakile Hare-haren Da Mayakan ISWAP Suka Kai Sansanonin Sojoji 5 A Borno
Dakarun soji na Operation HADIN KAI sun daƙile hare-haren da mayakan ISWAP suka kai kan sansanonin sojoji guda biyar a lokaci guda a wuraren Delwa da Goniri da Kukawa da Mainok da kuma wani matsugunin sojoji da ke dajin Sambisa na Jihar Borno a daren Lahadi 8 zuwa Litinin 9 ga Maris 2026.
Jaridar PRNIGERIA ta ruwaito cewa wannan na cikin sanarwar da Jami’in Yaɗa Labaran Operation HADIN KAI Laftanar Kanal Sani Uba ya fitar a ranar Litinin 9 ga Maris 2026.
Sanarwar ta bayyana cewa mayakan ISWAP sun kai hare-haren ne daga bangarori da dama a lokaci guda domin kokarin mamaye sansanonin sojojin.
Sai dai dakarun sojojin sun mayar da martani tare da samun goyon bayan karin dakaru da kuma bangaren jiragen yaki na Operation HADIN KAI wanda ya taimaka wajen dakile hare-haren.
Bayan artabun, sojojin hallaka wasu daga cikin su, sun kuma kwato wasu makamai da kayan yaki da ƴan taʼaddar suka bari yayin da suke arcewa.
Sai dai artabun ya lalata katangar tsaro a Goniri da Kukawa tare da lalata wasu gine-gine da motoci a sansanonin.
Sanarwar ta ce duk da hare-haren, sojojin Operation HADIN KAI na ci gaba da rike dukkan wuraren da aka kai harin, yayin da ake gudanar da karin bincike da sintiri a yankunan domin kamo mayakan da suka jikkata da suka tsere zuwa garuruwa makwabta.
Sai dai rundunar ta ce wasu sojoji sun rasu a yayin artabun.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
