Connect with us

News

Cutar Kwalara Ta Hallaka Akalla Mutum 74 A Borno 

Published

on

Zazzabin Lassa Cutar ta yi Ajalin Mutum 118 A Cikin Watanni Uku

Cutar kwalara da ta fara ɓarkewa a farkon watan Mayun 2026 a Jihar Borno da ke arewa maso gabashin Nijeriya ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 74 sannan wasu mutum 7,800 sun sake kamuwa, lamarin da ya yi wa cibiyoyin lafiya katutu, a cewar ƙungiyar agajin likitoci ta Médecins Sans Frontières (MSF).

MSF ta ce zuwa ranar 7 ga Yuni, an samu jimillar mutane 7,850 da ake zargin sun kamu da cutar a ƙananan hukumomi 14 na jihar, kamar yadda Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Borno ta bayyana. Ƙungiyar ta ce adadin masu kamuwa da cutar na ƙaruwa cikin sauri a kowace rana.

Advertisement

Titin Kiru–Yako Ya Zama Tarkon Mutuwa, Mazauna Yanki Sun Roƙi Gwamnatin Kano Ta Gaggauta Kammala Aikinsa

Ɓarkewar cutar na ƙara wa tsarin kiwon lafiya da tuni yake cikin mawuyacin hali nauyi, a yankin da ke fama da matsalolin tsaro sakamakon hare-haren masu tayar da ƙayar baya da kuma yawan mutanen da suka rasa matsugunansu, abin da ke ƙara haɗarin yaɗuwar cutar zuwa wasu wurare.

Advertisement

MSF, tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Borno, ta buɗe cibiyar kula da masu fama da kwalara a Maiduguri domin tallafa wa ƙoƙarin da ake yi na shawo kan annobar.

 

Advertisement

 

TRT AFRIKA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending