News
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
Wani matashi mai suna Ahmad Dankoli ya rasa ransa bayan wasu fusatattun matasa sun lakada masa duka har lahira tare da ƙona gawarsa kan zargin yunkurin satar babur a garin Balare da ke Ƙaramar Hukumar Ajingi a Jihar Kano.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:00 na daren Lahadi, lokacin da ake gudanar da kasuwar mako a garin.
Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Kotun Tafi-da-Gidanka Kan Masu Laifin Miyagun Ƙwayoyi
Ɗan majalisar gundumar Balare, Shu’aibu Abdulmumin Yalo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an zargi marigayin da ƙoƙarin satar babur mallakin wani ɗan kasuwa da ya halarci kasuwar.
A cewarsa, bayan an yi masa wannan zargi, matashin ya yi yunƙurin tserewa, amma wasu daga cikin mutanen da ke wurin suka bi shi, suka kama shi, sannan suka yi masa dukan kawo wuƙa kafin daga bisani su ƙona gawarsa.
Yalo ya ce jami’an tsaro sun isa wurin da lamarin ya faru domin ceto matashin da kuma dawo da doka da oda, sai dai yawan mutanen da suka taru ya hana su shawo kan lamarin.
Ya ƙara da cewa an dade ana fama da sace-sacen babura a kasuwar Balare, lamarin da ake ganin ya haddasa fushin jama’ar da ya kai ga wannan mummunan al’amari.
-
News4 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News5 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News4 days agoJami’an Ƴansanda Sun Kama Mahaifin Prince Adeyemi Adeniyi, Mutumin Da Ake Zargi Da Kafa Hukumar Bogi
