News
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
Wani matashi mai suna Ahmad Dankoli ya rasa ransa bayan wasu fusatattun matasa sun lakada masa duka har lahira tare da ƙona gawarsa kan zargin yunkurin satar babur a garin Balare da ke Ƙaramar Hukumar Ajingi a Jihar Kano.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:00 na daren Lahadi, lokacin da ake gudanar da kasuwar mako a garin.
Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Kotun Tafi-da-Gidanka Kan Masu Laifin Miyagun Ƙwayoyi
Ɗan majalisar gundumar Balare, Shu’aibu Abdulmumin Yalo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an zargi marigayin da ƙoƙarin satar babur mallakin wani ɗan kasuwa da ya halarci kasuwar.
A cewarsa, bayan an yi masa wannan zargi, matashin ya yi yunƙurin tserewa, amma wasu daga cikin mutanen da ke wurin suka bi shi, suka kama shi, sannan suka yi masa dukan kawo wuƙa kafin daga bisani su ƙona gawarsa.
Yalo ya ce jami’an tsaro sun isa wurin da lamarin ya faru domin ceto matashin da kuma dawo da doka da oda, sai dai yawan mutanen da suka taru ya hana su shawo kan lamarin.
Ya ƙara da cewa an dade ana fama da sace-sacen babura a kasuwar Balare, lamarin da ake ganin ya haddasa fushin jama’ar da ya kai ga wannan mummunan al’amari.
-
News6 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
Uncategorized2 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
