News
Walƙiya Tayi Ajalin Mata Biyu, Ciki Har Da Mai Juna Biyu A Bauchi
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi ta tabbatar da mutuwar mutane uku, ciki har da wata mata mai juna biyu da wata mai shayarwa, sakamakon walƙiya da ta auka wa wani gida a ƙauyen Gambiri da ke ƙaramar hukumar Bauchi.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Nafiu Habib, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce guguwar hadari da walƙiya ta kashe mutane uku a ƙauyen.
DSS Ta Kama Jami’in Bogi Da Kayan Hukumar A Abuja
Wani mazaunin yankin da ya bayyana sunansa da Abubakar Hussain ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:29 na yammacin ranar Litinin, lokacin da walƙiyar ta auka wa ɗakin da waɗanda abin ya shafa suke ciki.
Ya ce an binne waɗanda suka mutu da misalin ƙarfe 11 na safe ranar Talata.
A cewarsa, ɗaya daga cikin waɗanda suka mutu ita ce Hauwa Juli, wadda ta haihu kwanaki bakwai kacal kafin faruwar lamarin, tare da ’yarta mai suna Fatima.
Ya ƙara da cewa Habiba, wadda ke da juna biyu, ’yar uwar Hauwa Juli ce, yayin da jaririn da Hauwa ta haifa ya tsira daga lamarin.
Lamarin ya jefa al’ummar ƙauyen cikin jimami da alhini, yayin da aka dakatar da wasu harkokin zamantakewa da tattalin arziki saboda zaman makoki da mazauna yankin suka shiga.
-
News5 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
News6 days ago
An Tura Kwamishinonin ’Yansanda 30 Da Jami’ai 15,000 Domin Sanya Ido A Zaɓen Osun
-
News3 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
