Connect with us

News

Uba Ya Nemi Kotu Ta Tilasta Wa ’Yarsa Ta Fitar Da Mijin Aure A Kaduna

Published

on

kotu

Wani magidanci mai suna Lawal Hamisu ya shigar da ƙara a gaban Kotun Shari’a ta II da ke Magajin Gari a Jihar Kaduna, inda yake neman kotu ta umarci ’yarsa, Fatima Lawal, ta gabatar da mutumin da zai aure ta.

Ta bakin lauyansa, H.B. Debo, mai ƙarar ya shaida wa kotun cewa Fatima mai shekara 27 ta kammala karatun Babbar Difloma ta Ƙasa (HND), amma har yanzu ba ta gabatar da wani mutum da ya nemi aurenta a hukumance ba.

ICPC Ta Gano Ma’aikatan Bogi 908 A Wasu Ma’aikatun Gwamnatin Tarayya 50

Lawal ya ce duk da cewa ’yarsa tana da samari, babu wanda ya taɓa zuwa gidansu domin neman aurenta. Ya buƙaci kotun ta umarce ta da ta fito da wanda zai aure ta, sannan ta taimaka wajen ganin an ɗaura auren idan an cika sharuddan da suka dace.

Ya kuma yi zargin cewa mahaifiyar Fatima ce ta haddasa matsalar da ke tsakaninsa da ’ya’yansa.

A nata ɓangaren kuwa, Fatima ta musanta cewa tana da wanda ya nemi aurenta, tana mai cewa duk da kasancewar tana da abokai maza, babu wani da ya gabatar da kansa ga iyayenta a matsayin mai neman aurenta.

Advertisement

Da yake jawabi, Alƙalin kotun, Malam Yakubu Abdullahi, ya bayyana cewa shari’ar ta shafi dangantakar uba da ’yarsa, don haka tana buƙatar a yi taka-tsantsan kafin a yanke hukunci.

Alƙalin ya ce zai saurari kowanne ɓangare daban domin gano ainihin musabbabin rikicin kafin ya yanke hukunci.

Daga nan kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 3 ga Agusta, 2026.

 

 

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending