News
An Gurfanar Da Mutane Biyu Kan Zargin Tsoratar Da Dagaci A Kano
An gurfanar da Abubakar Isyaku da Aliyu Abdullahi a gaban Kotun Shari’ar Musulunci da ke Jaba, Kano, bisa zargin haɗa baki wajen aikata laifi da kuma tsoratar da Dagacin Gware na Ƙaramar Hukumar Wudil.
Mutanen biyu sun musanta zargin da ake yi musu a gaban kotun da Alkali Malam Mubarak ke jagoranta.
Dakarun Soji Sun Kuɓutar Da Mutane 23 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
Lauyar Aliyu, Barista Sahura Aliyu Abdullahi, ta nemi a ba shi beli, inda kotun ta amince da buƙatar bisa sharadin cewa ɗan uwansa da mai unguwarsa su tsaya masa.
Kotun ta ɗage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 21 ga Satumba, 2026.
Lauyar ta kuma bayyana cewa a baya Dagacin ya taɓa shigar da irin wannan ƙara a Kotun Majistare, amma daga bisani ya janye ta.
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News7 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
