News
Za A Saki Wadanda Ba Su Da Laifi Da Hannu A Yunkurin Juyin Mulki —Ministan Tsaron Najeriya
Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce za a saki mutanen da aka kama bisa zargin hannu a wani shirin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, idan bincike ya nuna cewa ba su da laifi.
Musa ya bayyana hakan ne yayin wata hira da Channels Television, inda ya ce hukumomin tsaro suna gudanar da bincike domin tabbatar da cewa ba a hukunta mutanen da ba su da hannu a lamarin ba.
Sarkin Yauri Ya Yaba Wa Gwamna Nasir Idris Bisa Ayyukan Ci Gaba A Masarautar
Ya ce wadanda aka tabbatar da cewa su ne manyan masu ruwa da tsaki a shirin ne kawai za a gurfanar da su gaban kotu.
Ministan ya kuma tabbatar da cewa zargin yunkurin juyin mulkin na gaskiya ne, yana mai cewa wadanda ake zargin sun yi niyyar aiwatar da shi. Ya ce DSS da NIA na ci gaba da bincike, yayin da wasu daga cikin wadanda aka kama tuni aka gurfanar da su a kotu.
An fara samun labarin zargin shirin juyin mulkin ne a shekarar 2025, bayan da aka kama wasu manyan jami’an soji bisa zargin karya dokokin aikin soja. Daga baya gwamnati ta shigar da kara kan wasu mutane da ake zargi da hannu a lamarin, da laifukan cin amanar kasa, ta’addanci da kuma safarar kudaden tallafa wa ta’addanci.
Musa ya bukaci ‘yan Najeriya su kare dimokuradiyya tare da magance matsalolin kasar ta hanyoyin dimokuradiyya.
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
