News
Gwamnatin Tarrayya Ta Ware Naira Bilyan 10 Domin Dakike Barazanar Cutar Ebola
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya kafa kwamitin don lura da kuma sa ido kan barazanar ballewar annobar Ebola a kasar.
Bayanin hakan na kunshe cikin sanarwar da maitaimakawa shugaban kasa kan yada labarai Bayo Onanuga ya fitar a yammacin ranar Talata.
Onanuga ya ce shugaba Tinubu ya ba da umarnin fitar da Naira Miliyan Dubu goma don fara tunkarar matsalar.
A cewarsa kudin zai taimaka wajen karfafa shirye-shirye na kar ta kwana.
Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Femi Gbajabiamila, ne zai jagoranci kwamitin, sai kuma mambobi daga maaikatar lafiya da kuma wakilan jihohi.
-
News4 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News5 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News4 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
