Connect with us

News

Guguwar Iska Mai Karfi Ta Hallaka Mutum 7, Yayin Da Fiye Da Mutum 5,400 Ke Cikin Mawuyacin Hali A Jigawa ‎

Published

on

images (2)

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA) ta ce mutum bakwai sun rasu, yayin da mutum 5,403 suka shiga cikin mawuyacin Hali sakamakon guguwar iska mai ƙarfi da ruwan sama da suka afku a sassa daban-daban na jihar.

‎Sakataren Zartarwa na hukumar, Hannafi Yakubu ne , ya shaida wa manema labarai a Dutse cewa lamarin ya shafi al’ummomi 120 da ke cikin ƙananan hukumomi 13 na jihar.

Farashin Mai Ya Tashi Bayan Trump Ya Janye Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Iran

‎A cewarsa, guguwar ta lalata makarantu 47 na gwamnati, cibiyoyin lafiya uku da kuma ofisoshin ‘yan sanda biyu. Ya ƙara da cewa an tattara waɗannan bayanai ne tun daga farkon daminar bana zuwa yanzu.

‎Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Dutse, Gwaram, Birnin Kudu, Kiyawa, Babura, Gumel, Kaugama, Ringim, Gagarawa, Kirikasamma, Sule Tankarkar, Miga da Buji.

‎Hannafi Yakubu ya ce gwamnatin jihar ta fara raba kayan agaji ga mutanen da lamarin ya shafa domin rage musu raɗaɗin halin dasuke ciki.

Advertisement

 

NAN

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending