Connect with us

News

Ku Fara Harbe Yan Bindiga Kafin Karbar Umarni — Ministan Tsaro Christopher Musa Ga  Dakarun Soji 

Published

on

Christopher Musa 1783030694

Ku Fara Harbe Yan Bindiga Kafin Karbar Umarni — Ministan Tsaro Christopher Musa Ga  Dakarun Soji

 

Ministan Tsaro, Christopher Musa, ya umarci jami’an tsaro da ke fafatawa da ’yan ta’adda da ’yan bindiga da kada su yi jinkirin ɗaukar mataki idan suka ci karo da masu ɗauke da makamai.

Ya ce duk jami’in da aka tura aiki amma ya ƙi fuskantar ’yan ta’adda ko ’yan bindiga da sunan yana jiran umarni, za a ɗauke shi tamkar yana taimaka wa maƙiya.

Mazauna Dorayi Karama Sun Roƙi Gwamnatin Kano Ta Kawo Musu Ɗauki Kan Matsalar Ambaliyar Ruwa

Christopher Musa ya bayyana hakan ne a birnin Sokoto yayin ƙaddamar da motocin sulke da sauran kayan aikin tsaro da gwamnatin jihar ta saya domin ƙarfafa yaƙi da matsalar rashin tsaro.

Advertisement

Ya jaddada cewa duk jami’in da aka tura bakin aiki yana da ikon kare kansa da kuma rayukan al’umma, don haka bai kamata ya jira wani sabon umarni kafin ya fuskanci ’yan bindiga ko ’yan ta’adda ba idan sun bayyana.

Ministan ya kuma buƙaci jami’an tsaron su yi amfani da sabbin kayan aikin yadda ya kamata, yana mai cewa gwamnati ta kashe kuɗaɗe masu yawa wajen samar da su domin ƙarfafa yaƙi da rashin tsaro a sassan ƙasar.

 

PUNCH

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending