Connect with us

Politics

Hadimin Gaduje Ya Fice Daga APC Zuwa ADC 

Published

on

FB IMG 1774260803090
Advertisements
Advertisements
Spread the love

Salihu Tanko Yakasai, daya daga cikin na hannun daman tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki zuwa ADC.

Yakasai ya sanar da ficewar ta sa ne a wani sako da ya wallafa a shafin sa na Facebook a safiyar yau Litinin.

Jami’an NDLEA Sun Kama Miyagun Kwayoyi Da Aka Ɓoye A Jaket Da Man Shafawa A Filin Jirgin Saman Legas

Advertisement

Ya kuma wallafa hoton katin jam’iyyar ADC da ya yi rijista a mazaɓarsa.

Ga sakon 👇 

Bayan shawarwari da tuntubar yan’uwa da abokan arziki da sauran yan gwagwarmayar siyasa abokan tafiya, mun yanke shawarar shiga Jam’iyar ADC Sabuwar Tafiya! Tuni, na mika takardar fita daga jam’iyar APC tare da yin rijista a sabuwar jam’iyar mu ta ADC.

Advertisement

Wanda suke da sha’awar shiga jam’iyar ADC zasu iya yin rijista ta wayar su a wannan link din www.adcregistration.ng cikin kankanin lokaci zaka samu katin ka na dan jam’iya!

Muna rokon Allah Ubangiji Ya sa hakan ne mafi alheri, Ya kuma sa jam’iyar ADC ta kafa gwamnati sama da kasa, Ya kuma sa hakan ya zama alheri ga yan Najeriya baki daya amin!

 

Advertisement

Salihu Tanko Yakasai

Dawisun Kanawa

Masoyin Kano da Arewa da Najeriya.

Advertisement

23rd March, 2026.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending