Politics
Peter Obi, Seyi Makinde sun halarci taron Kwankwaso
Babban ɗan siyasar nan na Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasar na Jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Rabiu Kwankwaso, ranar Lahadi ya karɓi baƙuncin takwarorinsa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar LP, Peter Obi da Gwamnan Jihar Oyo Seyi Makinde.
Da yake jawabi a wajen gangamin magoya bayan Kwankwaso, Peter Obi ya ce ya kai wa jagoran Kwankwasiyya ziyara ce domin yin gaisuwar Sallah da kuma nuna muhimmancin Kwankwaso a siyasar Nijeriya. Shi ma Seyi Makinde ya jinjina wa Kwankwaso.
HAWAN NASARAWA:Gwamnan Kano Ya Musanta Zargin Yin Watsi Da Sarki Sanusi II
Kwankwaso ya miƙa godiya bisa ziyarar tare da bayyana muhimmancin haɗin kai domin ci gaban Nijeriya.
Masana harkokin siyasa na ganin wannan ziyara na da alaƙa da fafutukar da ‘yan siyasar suke yi wajen ganin sun kawar da Jam’iyyar APC daga mulki a zaɓen 2027 mai zuwa.
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mai Safarar Makamai, Sun Kwato Harsasai 637 A Kaduna
-
News7 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News4 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
