Connect with us

News

Ƙasar Saudiyya Ta Sanar Da Shirinta Na Fara Bai Wa Miliyoyin Raƙuman Da Ke Ƙasar Fasfo

Published

on

e7af4733 ae14 451e 9ce9 f47880c7c69d.jpg
Spread the love

Ƙasar Saudiyya ta sanar da shirinta na fara bai wa miliyoyin raƙuman da ke ƙasar fasfo, domin inganta kula da su da kuma sauƙaƙa tsarin gudanar da muhimmin fannin kiwon raƙuma.

Jami’ai sun ce wannan mataki zai taimaka wajen ƙara yawan amfanin fannin, da inganta inganci, tare da samar da sahihin kundin bayanai da za a rika dogaro da shi wajen tantance shaida da mallakar raƙuma.

Yan Bindiga Sun Sace Uwa Mai Shayarwa Da Yara 6 A Edo

Wani saƙo da ma’aikatar muhalli, ruwa da noma ta wallafa a shafukan sada zumunta ya nuna hoton fasfon, wanda ke da launin kore, tare da tambarin ƙasar da kuma hoton raƙumi mai launin zinariya.

Advertisement

A shekarar 2024, gwamnatin Saudiyya ta ƙiyasta cewa akwai kusan raƙuma miliyan biyu da dubu dari biyu a ƙasar.

Saudiyya kuma na shirya gasar kyau na raƙuma a lokacin bukukuwan shekara-shekara, lamarin da ke nuna muhimmancin raƙumi a al’adu da tattalin arziƙin ƙasar.

 

BBC HAUSA

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *