News
An Ƙara Kuɗin Yin Fasfo A Najeriya
Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS) ta sanar da cewa daga ranar 1 ga watan Satumba, 2025, za a ƙara kuɗin yin fasfo na ƙasar.
A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, ACI AS Akinlabi, ya fitar a ranar Alhamis, ya ce ƙarin zai shafi masu neman fasfo a Najeriya ne kawai.
Cutar Amai Da Gudawa Ta Kashe Mutane Takwas A Zamfara, Fiye Da 200 Sun Kamu
Sanarwar ta bayyana cewa fasfo mai shafi 32 zai koma N100,000, yayin da na shafi 64, wanda zai yi shekara goma kafin ƙarewa, zai koma N200,000.
Sai dai kuɗin da ’yan Najeriya mazauna ƙasashen waje ke biya bai canza ba – ana ci gaba da cajin Dala 150 ga fasfo mai shafi 32 da Dala 230 ga na shafi 64.
Hukumar ta ce wannan ƙarin kuɗin na cikin shirin da aka ɗauka don ƙara inganci da tsaron fasfo, tare da tabbatar da cewa ya ci gaba da samuwa ga ’yan ƙasa.
