News
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Dalibar Da Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya Da Kyautar Naira 200,000
Gwamnatin tarayya ta bai dalibar nan da ta lashe gasar turanci ta duniya ta TeenEagle, Nafisa Abdullahi, kyautar N200,000.
Ministan Ilimi Dr. Tunji Alausa ne ya bayar da kyautar gare ta a lokacin wani kwarya-kwaryan shagali da aka shirya musu a yau Alhamis a Abuja.
Idan ba a manta ba dai gidauniyar Atiku ta baiwa zakarun TeenEagle wato Nafisa Abdullahi, Rukaiya Fema, da Khadija Kalli tallafin karatu sakamakon bajintar da suka yi a gasar TeenEagle ta Duniya.
Advertisements
