News
Matar Da Ta Haifi ‘Ya ‘Ya Biyar A Asibitin Murtala Ta Rasu.
Rahotanni daga Jihar Kano sun tabbatar da rasuwar matar nan da ta haifi jarirai biyar a Asibitin Kwararru na Murtala.
Majiyoyi sun bayyana cewa matar, wadda ta haihu a jiya, ta rasu ne a daren Laraba bayan da aka ce tana karbar kulawar likitoci sakamakon yanayin haihuwar da ta bukaci kulawa ta musamman.
HAJJIN 2026: Sama Da Maniyyata 1,000 Sun Rasa Bizar Zuwa Hajji A Kaduna
Rasuwar ta zo ne cikin yanayi mai tada hankali, musamman ganin yadda labarin haihuwar jariran biyar ya dauki hankalin al’umma a jihar da ma kasa baki daya.
Ya zuwa yanzu, ba a samu cikakken bayani daga hukumomin lafiya ba kan ainihin musabbabin rasuwar, yayin da ake sa ran za a fitar da karin haske kan lamarin.
A halin yanzu, hankula sun karkata kan lafiyar jariran biyar din, wadanda ake ci gaba da kula da su a asibitin.
