Connect with us

News

Matar Da Ta Haifi ‘Ya ‘Ya Biyar A Asibitin Murtala Ta Rasu.

Published

on

FB IMG 1774519732426
Advertisements
Advertisements
Spread the love

Rahotanni daga Jihar Kano sun tabbatar da rasuwar matar nan da ta haifi jarirai biyar a Asibitin Kwararru na Murtala.

Majiyoyi sun bayyana cewa matar, wadda ta haihu a jiya, ta rasu ne a daren Laraba bayan da aka ce tana karbar kulawar likitoci sakamakon yanayin haihuwar da ta bukaci kulawa ta musamman.

HAJJIN 2026: Sama Da Maniyyata 1,000 Sun Rasa Bizar Zuwa Hajji A Kaduna

Advertisement

Rasuwar ta zo ne cikin yanayi mai tada hankali, musamman ganin yadda labarin haihuwar jariran biyar ya dauki hankalin al’umma a jihar da ma kasa baki daya.

Ya zuwa yanzu, ba a samu cikakken bayani daga hukumomin lafiya ba kan ainihin musabbabin rasuwar, yayin da ake sa ran za a fitar da karin haske kan lamarin.

A halin yanzu, hankula sun karkata kan lafiyar jariran biyar din, wadanda ake ci gaba da kula da su a asibitin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending