News
Jam,iyyar labour party tayi Kira da gwamnatin Jahar legas akan inganta albashin ma,aikata
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Jam’iyyar Labour reshen jihar Legas ta roki Gwamna Jahar Babajide Sanwo-Olu da ya tabbatar da biyan albashin ma’aikata
Sakatariyar yada labaran jam’iyyar ta jihar Legas, Mrs. Olubunmi Odesanya, ta yi wannan roko a wata tattaunawa da ta yi da kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ranar Laraba
Odesanya, tayi wannan Kira ne daidai lokacin da Sanwo-Olu da yake bikin cikar shekara ta farko da cikar wa’adin mulkinsa na biyu
,
tace akwai bukatar gwamnan ya kara zage damtse wajen sauke nauyin sa da ke kan mazauna yankin daga kalubalen zamantakewa da tattalin arziki.
A cewarta, talakawan jihar da suka hada da ma’aikata na kokawa da rayuwa da kuma biyan bukatun su na yau da kullum da na iyali.
Ta kuma bukaci jam’iyyar APC mai mulki da ta baiwa ma’aikata damar yin duk abin da ta gabatar a matsayin mafi karancin albashi.
Odesanya tace jama’a na bukatar albashin rayuwa, wanda zai dauki ilimin zamantakewa da tattalin arziki don ma’aikata su yi farin ciki.
Ta ce: “Dukkanmu muna kallo cikin fargabar rashin biyan albashi . Mafi karancin albashi na yanzu Yana karbar N30,000 ya kamata a sake duba shi a wannan shekara ta 2024, kamar yadda za mu iya tunawa, daga yarjejeniyar da aka amince da ita da kuma rubutacciyar dokar aiki. A al’ada, bai kamata ya haifar da tsoro ko fushi ba amma don matsalolin ƙasar. ”
Shugaban jam’iyyar Labour tace akwai bukatar gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar da su baiwa ma’aikatan su albashi Mai kwari
Ta ce nan take cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi ya sa farashin kayayyaki da na masarufi ya kai matakin da bai taba kaiwaba
