Connect with us

News

Gobara Ta Kone Wasu Shaguna a Kasuwar Kofar Wambai Dake Birnin Kanon Dabo

Published

on

FB IMG 1740914174850
Spread the love

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Rahotanni sun bayyana cewa wata gobara da ta tashi da safiyar yau Lahadi ta kone wasu shaguna a kasuwar Kofar Wambai dake birnin Kano.

Wutar ta tashi ne da misalin karfe 5 na Asubahin yau, a Layin ‘yan Kabeji, kusa da shagunan masu siyar da kayan gwanjo. Shaidu sun bayyana cewa gobarar ta fara ne daga wani shago kafin ta fara bazuwa zuwa wasu shaguna dake makwabtaka.

Yan-sanda Sun Kama Magidanci Da Ya Kashe Matarsa Kan Abincin Buda Baki A Bauchi

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta isa wurin domin dakile wutar, yayin da har yanzu ba a tantance musabbabin tashin gobarar ba, haka kuma ba a bayyana adadin asarar da aka tafka ba.

Advertisement

Wasu ‘yan kasuwa sun bayyana damuwarsu kan yadda gobara ke ci gaba da afkuwa a kasuwannin jihar, suna mai kira ga hukumomi da su kara daukar matakan kariya.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *