Interview
Masarautar Daura Ta Nada Sarautu Ga Wadanda Suka Hidimta Wa AL-QUR’ANI Da Almajirrai
Daga Mukhtar A. Haliru Tambuwal, Sokoto
Masarautar Daura da ke jihar Katsina ta nada sarautu biyu ga wasu bayin Allah da suka yi fafutuka wajen tabbatar da hakkokin almajirai da makarantun tsangaya.
Tsohon dan majalisar tarayya daga Sokoto, Hon. Dr. Balarabe Shehu Kakale, an ba shi sarautar Barden Makarantun Tsangaya da Makarantun Allo na Kasar Hausa. Haka kuma, Hajiya Aisha Jibril Dikku an nada ta matsayin Sarauniyar Tsangayu da Makarantun Allo.
Nadin sarautar ya gudana ne tare da wasu nade-nade a fadarsa Mai Martaba Sarkin Daura, Alh. Dr. Umar Farouk Umar CON. A yayin bikin, Sarkin Daura ya bayyana cewa:
“Duk inda Tsangayun Makarantun Allo suke a ƙasar Hausa da kuma jihohi goma sha tara (19) na Arewacin Najeriya, mun umurce ka da ka wakilce mu.”
An nada wadannan bayin Allah ne domin su taka rawar gani wajen ci gaba da kare hakkokin almajirai. A lokacin da suke majalisar dokoki, sun yi aiki tukuru har aka sanya dokar kare hakkin almajirai da yaran da ba su karatu hannu. Wannan dokar ce ta ba da damar kafa hukuma mai kula da inganta karatun tsangaya da almajirai a Najeriya, wadda ake cin moriyarta a yau.
Sabon Barden Makarantun Tsangaya da Makarantun Allo, Hon. Dr. Balarabe Shehu Kakale, ya nuna matukar godiyarsa ga Masarautar Daura bisa wannan girma da aka yi masa. Ya kuma godewa duk wadanda suka halarta daga ciki da wajen Daura, har ma da makwabtan kasashe kamar Maradi a Nijar da Senegal.
Bayan kammala nadin sarautar, an yi hawan daba tare da kai ziyara ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
