Opinion
Har Yanzu ‘Yan Najeriya Na Jira Bayani Daga Peter Obi Kan Kalamansa Game da IPOB
Daga Kwamared Najeeb Nasir Ibrahim
Jagoranci ba wai yin alkawura kawai ba ne, har ila yau yana tattare da ɗaukar alhakin kalaman da mutum ya yi a bainar jama’a. Duk ɗan siyasar da ke neman jagorantar ƙasa mai ɗimbin al’umma da bambance-bambance irin Najeriya, wajibi ne ya yi taka-tsantsan da kalamansa, musamman idan suna da alaƙa da tsaro, haɗin kan ƙasa da walwalar jama’a.
Shekaru bayan kalaman da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi, ya yi cewa mambobin IPOB ba ‘yan ta’adda ba ne, kuma yana rayuwa tare da su ba tare da jin tsoro ba, har yanzu ‘yan Najeriya na jiran cikakken bayani daga gare shi kan wannan matsaya.
Tsadar Gas Ya Tilasta Wa Mazauna Kano Komawa Amfani Da Gawayi Da Itacen Girki
Batun ba ƙaramin al’amari ba ne da za a iya wucewa kawai. Lamari ne da ya shafi haɗin kan ƙasa da kuma amincin duk wanda ke neman shugabantar Tarayyar Najeriya.
Tambayar da ke gaban ‘yan Najeriya a yau ita ce: Shin Peter Obi har yanzu yana tsayawa kan waɗannan kalamai nasa?
Idan har matsayinsa bai canza ba, wajibi ne ya yi cikakken bayani ga jama’a. Idan kuma ya sauya ra’ayi, ya kamata ya fito fili ya bayyana sabon matsayinsa. Yin shiru ba zai wadatar ba a kan batu da ya daɗe yana jawo muhawara a fagen siyasa da tsaron ƙasa.
Masu neman shugabanci ba za su iya zaɓar lokacin da za su yi magana kan wasu batutuwa ba, sannan su guje wa amsa tambayoyi masu muhimmanci idan suka taso. ‘Yan Najeriya sun cancanci fiye da kalaman yaƙin neman zaɓe; suna buƙatar amsoshi masu gamsarwa da bayyananniyar matsaya.
A lokuta da dama, jama’a sun sha ganin wasu shugabannin siyasa suna Allah-wadai da matsalar tsaro a wani lokaci, amma kuma a wani lokacin su yi kalaman da ke haifar da tambayoyi ko ruɗani game da matsayinsu. Irin wannan yanayi na iya rage amincewar jama’a da shugabanni.
Duk wanda ke neman zama shugaban ƙasa ya kamata ya kasance a shirye ya kare tarihin siyasarsa, ya yi bayani kan kalamansa, tare da amsa tambayoyin da jama’a ke da haƙƙin yi.
Wannan ba hari ba ne kan Peter Obi a matsayinsa na mutum. Kira ne gare shi a matsayin fitaccen ɗan siyasa. Dimokuraɗiyya tana buƙatar a riƙa tantance shugabanni da kalamansu. Neman bayani ba tsangwama ba ne, kamar yadda yin tambayoyi ba ƙiyayya ba ne.
Magoya bayan Peter Obi sun sha bayyana cewa yana wakiltar sabuwar siyasa mai cike da gaskiya da riƙon amana. Idan haka ne, to bayyana matsayinsa a fili bai kamata ya zama abin wahala ba. Shugaban da ke neman amincewar sama da mutane miliyan 200 ya kamata ya kasance a shirye ya fuskanci tambayoyi masu wahala kai tsaye, maimakon barin jita-jita da ce-ce-ku-ce su ci gaba da yawo.
A halin da Najeriya ke ciki na ƙalubalen tsaro, matsin tattalin arziki, rashin aikin yi ga matasa da kuma raguwar amincewa da cibiyoyin gwamnati, ƙasar na buƙatar shugabanni masu magana da murya ɗaya, daidaitacciyar matsaya da kuma cikakken yakini.
A yanzu, nauyin yana kan Peter Obi ya bayyana wa ‘yan Najeriya inda yake tsaye kan wannan batu. Ba ta bakin wakilai ba. Ba ta hanyar fassarar da ake yi a kafafen sada zumunta ba. Ba ta hanyar zaɓen wasu kalamai kaɗai ba. Jama’a na son jin matsayinsa kai tsaye daga gare shi.
Najeriya ba za ta iya ci gaba da tafiya bisa zato da hasashe ba. Jagoranci na buƙatar bayyananniyar matsaya. Riƙon amana kuma na buƙatar amsoshi. Kuma a kan wannan batu, har yanzu ‘yan Najeriya na jira.
Kwamared Najeeb Nasir Ibrahim shi ne Darakta Janar na The Unifier Project, kuma yana rubuce-rubuce kan harkokin mulki, dimokuraɗiyya da al’amuran ƙasa
