Connect with us

News

Kwankwasiyya Ta Yi Allah-wadai Da Kalaman Da Asari Dokubo Ya Yi Kan Kwankwaso

Published

on

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta yi Allah-wadai da kalaman da Asari Dokubo ya yi kan jagoranta, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tana mai cewa kalaman na cike da rashin tushe kuma na iya haddasa rarrabuwar kai.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƙungiyar, Dakta Habibu Sale Mohammed, ya fitar, ya ce zargin da Dokubo ya yi ba gaskiya ba ne, kuma an yi shi ne domin karkatar da hankalin jama’a daga muhimman batutuwan da ke gaban ƙasa.

Advertisement

Sanarwar ta ce zargin cewa Kwankwaso zai iya “sayar da Musulmi kan kobo-kobo” magana ce mai zafi wadda ba ta dace ba, tare da jaddada cewa tarihin siyasar sa ya nuna kishin al’umma da adalci ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.

Kwankwasiyya ta ce ya kamata a rika auna shugabanci bisa ayyukan da aka gani a fili, musamman a bangarorin ilimi, ci gaban ababen more rayuwa da kuma shugabanci mai haɗa kai.

Advertisement

Ƙungiyar ta kuma bayyana cewa irin waɗannan kalamai na iya zama wata hanya ta karkatar da hankalin jama’a daga matsalolin da ke addabar ƙasa, ciki har da tsadar rayuwa, rashin tsaro da kuma talauci.

Ta ƙara da cewa ba za ta shiga muhawarar zagi da cin mutunci ba, amma za ta ci gaba da kare martabar jagoranta.

Advertisement

A ƙarshe, ƙungiyar ta yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji siyasar ƙiyayya da yaɗa bayanan da ba su da tushe, tare da rungumar haɗin kai da tattaunawa mai amfani.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending