News
Jihar kano zata kara rike kanbunta ta uwa a Arewa Idan aka habbaka harkokin Tarihi da Al’ada -bashir Hayatu jantule
DAGA IBRAHIM AMINU
Kwararan Dan siyasar nan a jahar kano bashir Hayatu jantule yace jahar kano zata kara rike kanbunta ta uwa a Arewa Idan aka habbaka harkokin Tarihi da Al’ada
Ya bayyana haka ne a lokacin da yakai ziyara ofishin sakataren gudanarwa na hukumar kula da Tarihi da al’adu a jahar kano watao Arc. Ahmed Abba Kabir Yusuf.
A wajena kama ta ke yi da budurwa sharaf”, Cewar matashi mai soyayya da dattijuwa.
Wanda gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Eng Abba kabir Yusuf ta nadashi
Jantule ya kara da cewa kasan cewar Ahmed a wannan waje ba karamin cigaba zai kawowa jahar kano ba ta yadda yace dama cen dan gidan ne daga nan yafito kuma yasan zai yi iya kokarin na dan yaga ya kara ingantata fiye da yadda yasame ta a yanzu.
Ya kara da bashi shawara cewa ya kamata yabawa mara da kunya kuma yasani yanada kalubale masu tarin yawa kasan Cewar sa dan uwa ga shi mai girma Gwamna.
Daga karshe ya nuna jin dadinsa ga wannan dama da ya samu kuma dolene suma suci gaba da bashi shawara ta gari.
