News
Tinubu ya taya Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano murnar cika shekaru 61 a duniya.
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya taya Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano murnar cika shekaru 61 a duniya.
A wata sanarwa ta bakin Ajuri Ngelale, mashawarcin shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Tinubu ya amince da tsayuwar daka a siyasar Gwamna Yusuf, inda ya tashi ta hanyar siyasa tun daga mataimaki na musamman zuwa kwamishina kuma a yanzu.
Shugaban na yi wa Gwamnan fatan samun nasarar gudanar da ayyukan sa.
Shugaban ya kuma yi addu’ar Allah ya kara wa Gwamna shekaru masu yawa cikin koshin lafiya.
Advertisements
