Connect with us

News

Ya kamata Gwamnatin Tarayya Ta Gaggauta Janye Karin Kudin Wutar Lantarki – SERAP  

Published

on

DAGA HASSAN KHALID HAMZA 

 

Advertisement

 

Kungiyar kare ‘yancin harkokin zamantakewa da na tattalin arziki ta SERAP, ta buƙaci Shugaba Muhammadu Buhari da ya yi gaggawar janye ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi ba bisa ka’ida ba a watan Disamban 2022.

Advertisement

 

Kungiyar ta bukaci shugaban kasa da ya umarci ministan wutar lantarki, Goddy Jedy-Agba da shugaban hukumar kula da hasken wutar lantarki ta Najeriya (NERC), Farfesa James Momoh da su gaggauta janye karin kudin wutar lantarkin.

Advertisement

Jaruman Kannywood Da Suka yi Aure A shekara 2022

A wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, Mataimakin Daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ya bukaci Buhari ya “tabbatar da binciken kashe kuɗaɗen jama’a a matsayin ‘zuba jari da ceto’ da gwamnatocin baya suka yi wa kamfanonin rarraba wutar lantarki (DisCos) da kamfanonin samar da wutar lantarki (GenCos) tun 2005 da kuma gurfanar da wadanda suke da hannu gaban kuliya.

 

Advertisement

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa biyo bayan amincewar da Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya ta bayar, an kara kudin wutar lantarki a fadin kamfanin rarraba wutar lantarki na kasar nan a watan Disambar 2022. Wasu kwastomomin da dama sun tabbatar da karin kudin.

 

Advertisement

Ministan wutar lantarki da NERC duk sun ki tabbatarwa ko musanta ƙarin kudin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending