News
’Yan Bindiga Sun Sace Gomman Fasinjojin Jirgin Kasa A Edo
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
Wasu ’yan bindiga sun yi awon gaba da fasinjoji da dama a wata tashar jirgin kasa da ke karamar hukumar Igueben a Jihar Edo.
Wadanda abin ya rutsa da su dai na dakon shiga jirgin kasa ne zuwa Warri da ke Jihar Delta a lokacin da maharan suka far musu.
Dakarun Rasha sun kakkaɓo wani jirgi maras matuƙi a garin Sevastopol na Ukraine
Kawo yanzu dai babu tabbas ko wani ya mutu a lamarin amma matafiyan da dama sun samu raunuka kamar yadda jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a Edo, Chidi Nwabuzor, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Jami’in ya ce masu garkuwa da mutane dauke da bindigogi kirar AK 47, sun mamaye tashar jirgin ne da Yammacin ranar Asabar, inda suka rika harbi a iska kafin su yi awon gaba da matafiya da dama.
Harin na zuwa ne kasa da shekara guda bayan da ’yan ta’addan suka kaddamar da hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna inda suka kashe wasu fasinjojin jirgin tare da yin garkuwa da sama da 60 daga cikinsu.
Lamarin ya tilasta wa Gwamnatin Tarayya dakatar da sufurin jirgin kasa a hanyar Abuja zuwa Kaduna sama da watanni shida kafin maido da shi baya-bayan nan.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
