News
An Hallaka Matashin Da Ya Kai Wa Sheikh Musa Lukuwa Hari A Sakkwato
Rundunar ’yan sandan Jihar Sakkwato ta tabbatar da mutuwar wani matashi da ake zargi da kai wa fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Musa Lukwa, hari bayan kammala sallar Juma’a.
Kakakin rundunar, DSP Ahmad Rufa’i, ya bayyana cewa wasu daga cikin mabiyan Sheikh Lukwa ne suka cafke matashin da ake zargin, kafin daga bisani su kashe shi.
Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wani Mutum Bisa Zargin Satar Wayar Hannu Guda 41 A Maiduguri
Ya ce Sheikh Musa Lukwa na ci gaba da karɓar magani a Asibitin Kwararru na Sakkwato, sakamakon raunukan da ya samu a yayin harin.
DSP Rufa’i ya ƙara da cewa kawo yanzu rundunar ba ta kama wani mutum dangane da tashin hankalin ba, sai dai ta ɗauki matakan tsaro domin hana lamarin ƙara ta’azzara.
Ya ce jami’an tsaro sun fara gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin harin, tare da gano duk mutanen da ake zargin suna da hannu a lamarin.
