Connect with us

News

Kungiyar Hezbollah da Isra’ila sun yi musayar wuta yayin da ake fuskantar tashin hankali a kan iyaka

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Advertisement

Kungiyar Hizbullah ta Lebanon da Isra’ila sun yi musayar wuta a daidai lokacin da ake ci gaba da samun tashin hankali a kan iyakar Lebanon da Isra’ila.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hezbollah ta ce ta kai hari kan wata na’urar radar a kudancin Lebanon da “makaman da suka dace”, wanda kuma ya samu inda ake so “kai tsaye.”

Advertisement

Rusau A Filin Idi : Kotu Ta Bada Umarni A Rufe Asusun Gwamatin jahar Kano Guda 20 A Najeriya

A nata bangaren, rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kai hare-hare a wurare da dama a kudancin kasar Lebanon, a matsayin martani ga hare-haren da kungiyar Hizbullah ta kai kan wuraren sojin Isra’ila.

 Trt Afirka ta ruwaito cewa a ce ta gano wasu makamai masu linzami da aka harba daga Lebanon zuwa wani sansanin soji da ke kusa da kauyen Arab al Aramshe da ke yammacin Galili da kuma wani shingen tsaro a yankin Hermon.

Advertisement

A wani labarin kuma Rusau A Filin Idi : Kotu Ta Bada Umarni A Rufe Asusun Gwamatin jahar Kano Guda 20 A Najeriya

Ma’aikatar Lafiya da ke Gaza ta tabbatar da cewa an kai gawawwakin mutum 73 da kuma mutum 123 wadanda suka samu rauni asibitin Al-Aqsa a sa’o’i 24 da suka gabata.

Advertisement

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare a fadin Falasdinu ba kakkautawa.

Kasashen duniya da dama na ci gaba da Allah wadai da kan kisan da Isra’ila ke yi a Gaza.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending