Connect with us

Sports

Da kyar idan Pogba zai buga gasar kofin duniya a Qatar

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Za a yi wa dan wasan Faransa mai taka leda a Juventus, Paul Pogba tiyata a gwiwar kafarsa, watakila ba zai buga gasar kofin duniya da za a yi a Qatar a bana ba kenan.

 

Advertisement

Pogba mai shekara 29 ya ji raunin a cikin watan Yuni, wanda kawo yanzu bai buga wasa ba tun fara kakar 2022/23.

 

Advertisement

Faransa za ta fara wasan kare kofinta, inda za ta kece raini da Australia ranar 22 ga watan Nuwambar 2022.

 

Advertisement

“A safiyar nan Pogba ya yi atisaye a karo na biyu, amma sai tsayawa ya yi, hakan ya sa muka yanke shawarar yi masa tiyata,” in ji kociyan Juventus Massimiliano Allegri.

 

Advertisement

Muna sa ran watakila ya dawo buga tamaula a cikin watan Janairu.”

 

Advertisement

Za a dakatar da wasannin Serie A daga ranar 13 ga watan Nuwamba domin buga kofin duniya, daga baya a ci gaba da fafatawa cikin Janairu.

 

Advertisement

An tambayi kociyan ko Pogba zai iya buga wa Faransa kofin duniya, Allegri ya kara da cewar ”Gasar kofin duniya ba matsala ta bace, kalubalen Juventus ya koma buga tamaula a cikin watan Janairu.”

 

Advertisement

Pogba ya sake komawa kungiyar da ke buga Serie A da taka leda a kakar nan, bayan da kwantiraginsa ya kare a Manchester United.

 

Advertisement

Dan wasan ya ci kwallo a karawar da Faransa ta doke Croatia 4-1 ta kuma lashe kofin duniya a Rasha a 2018 na biyu da ta dauka jumulla kenan

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

BBC NEWS

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending