News
Ganduje Ya Sha Alwashi Sai An Hukunta Dan Chinan Da Ya Yi Ajalin Budurwarsa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ce lallai za’a dauki matakin Shari’a akan dan kasar China da ya kashe tsohuwar budurwar sa mai suna Ummulkairi Sani a unguwar Dorayi Babba a karamar hukumar Gwale.
Ganduje ya Bayyana Hakanne a wajen Bikin Kaddamar da Sabbin Kwamitocin Hukumar Shari’a ta Jihar kano da Hukumar zakka da Hukumar Hisbah wanda aka yi a dakin taro na Coronation Hall dake fadar gwamnatin kano.
Wadanne Shugabannin Duniya Aka Gayyata Bikin Binne Sarauniya Elizabeth II?
Gwamna Ganduje ya ce “Mun sami labarin dan kasar China da ya kashe wata budurwar sa, lamarin bai mana dadi ba sam kuma akwai abun bakin ciki”
“Kuma lallai baza’a bar shi haka ba, mun sa an kama shi domin hukunta shi akan abun da ya aikata”.
Ma’aikatar Shari’a akwai babban aiki a gaban ku game da wannan lamarin” a cewar gwamna Ganduje.
Gwamnan ya kuma addu’ar Allah ya ji kan ta da gafara.
