Connect with us

News

Sojin saman Najeriya sun kashe ‘yan bindiga a Zamfara

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Rundunar sojin sama ta Najeriya ta ce hare-hare ta sama da ta ke kai wa maboyar ‘yan bindiga sun hallaka gwammansu a jihar Zamfara da ke arewacin kasar.

 

Advertisement

Samame ta sama da sojin suka kai karamar hukumar Maru a karshen mako, ya biyo bayan munanan hare-haren da ‘yan bindiga suka kai kauyukan da ke yankin.

Netherlands ta nemi gafara akan bautar da bakaken fata

Mazauna kauyukan da ke yankin sun shaidawa BBC cewa matsawar jami’an tsaron Najeriyar ta tilastawa ‘yan bindigar da ke garkuwa da mutane, arcewa wani kauye mai suna Mutunji, inda nan ma akai muu luguden wuta.

Advertisement

 

Mazauna kauyukan sun kuma ce, sun ga gawawwakin ‘yan bindigar har guda 60, da wasu 20 da suka jikkata, sai kuma baburan maharan da sojojin suka lalata.

Advertisement

 

Sai dai sun ce akwai tsirarun farar hula da lamarin ya rutsa da su, ciki har da wau tsofaffi da ke kokarin tserewa a lokacin da gungun ‘yan bindigar akan babura da manyan makamai suka tunkaro kauyensu domin gujewa samamen da luguden wuta ta saman da sojojin Najeriyar ke yi babu kakkautawa.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending