Connect with us

News

Tsawa Ta Kashe Masu Garkuwa Da Mutane Su 3 A  Jihar Kwara

Published

on

DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA

Tsawa ta kaseh wasu mutum uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne domin neman kudin fansa a garin Oro Ago da ke Karamar Hukumar Ifelodun ta Jihar Kwara.

Advertisement

Amimiya ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne ranar Litinin.

Kotu Ta Daure Matashi Shekara 2 Bisa Damfara Da Sunan Sojan Amurka

A cikin wani bidiyo mai tsawon dakika 30, wanda ya karade kafafen sada zumunta, an ga gawarwakin mutanen su uku sun kone kurmus ba a iya gane su, ga kudaje kuma suna bin su.

Advertisement

Wata murya kuma a kan bidiyon na cewa, “Mu ne ’yan kwamitin bijilan na Igbomina. Kokarin da muke yi na yaki da batagarin da ke aikata ayyukan masha’a a wannan yankin ya fara haifar da da mai ido.

“Tsawa ta kashe wasu da ake zargin masu garkuwa ne su uku. Allah zai ci gaba da taimakon mu a kan duk masu nufinmu da sharri a yankinmu,” in ji muryar.

Advertisement

Mazauna yankin dai sun yi zargin cewa wadanda suka mutun suna cikin wani ayarin masu garkuwa su takwas da suka kai hari yankin Iwo da ke Karamar Hukumar Isin, mako biyu da suka gabata.

A yayi harin na wancan lokacin dai, an kashe wani basarake sannan, sannan aka sace wani jagoran Kiristoci na yankin.

Advertisement

Wani dan kungiyar ci gaban garin Oro-Ago da ya bukaci a sakaya sunansa, ya shaida wa Aminiya cewa Allah ne Ya kai tsawar domin ta tallafa musu, amma babu hannun wani mutum a ciki.

Shi kuwa Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Ebunoluwarotimi Adelesi, ya ce tuni jami’ansa sun fara bincike a kan lamarin.

Advertisement

Sai dai ya ce ba za su iya tantance asalin abin da ya haddasa tsawar ba, sai nan gaba.

A wani labarin kuma Kotu Ta Daure Matashi Shekara 2 Bisa Damfara Da Sunan Sojan Amurka

Advertisement

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

Advertisement

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending