Connect with us

News

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Kano Ta Saka Ranar Komawa Makarantar Firamare Da Sakandire

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da ranar Lahadi 15 ga watan Satumba a matsayin ranar komawa makaranta ga daliban makarantun kwana na gwamnati da masu zaman kansu a jihar domin fara karatun zangon karatu na 2024/2025.

Advertisement

Yayin da daliban makarantun jeka-ka-ka-dawo a fadin jihar zasu koma makaranta a ranar Litinin, 16 ga watan na Satumba.

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Tsawaita Wa’adin Ma’aikan Jihar 4,000 Da Ganduje Ya Yi

Idan za a iya tunawa dai, a ranar Asabar 7 ga watan Satumba ne, kwamishinan ilimi, Alhaji Umar Haruna Doguwa ya sanar da dage ranar komawa makarantar.

Advertisement

A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labarai na ma’aikatar ilimi, Balarabe Abdullahi Kiru, ya bukaci iyaye da su tabbatar da dalibai sun koma makarantun su a ranar.

Sanarwar ta kuma bukaci, dalibai da su kaucewa kawo haramtattun abubuwa zuwa makarantar kamar su wukake da Reza kuma su kasance masu bin doka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending