Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Juma’a A Matsayin Ranar Hutu

Published

on

Gwamnatin Tarayya  ta ayyana ranar Juma’a mai zuwa a matsayin ranar hutu ga ma’aikata a fadin ƙasar, domin bikin Ranar Ma’aikata ta Duniya.

Sanarwar ta fito ne daga Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ta bakin Babbar Sakatariyar ma’aikatar, Magdalene Ajani, a yau Laraba a Abuja.

Advertisement

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Sababbin Shugabannin Jam’iyyar ADC Tsagin David Mark Suka Zaba A Jihohi

A cewar sanarwar, an ɗauki wannan mataki ne domin bai wa ma’aikata damar yin bikin ranar da ake warewa domin girmama rawar da suke takawa wajen gina tattalin arziki da ci gaban ƙasa.

Advertisement

Ministan ya yabawa ma’aikatan Najeriya bisa jajircewa da ƙwazon aiki, yana mai jaddada cewa gudummawar su na da matuƙar muhimmanci ga bunƙasa da wadata ƙasa.

Haka kuma, ya bukaci su da su ci gaba da nuna kwarewa da sadaukar da kai a ayyukansu domin ci gaban Najeriya baki ɗaya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending