Connect with us

News

Da Ɗumi Ɗumi: Khalifa Muhammadu Sunusi II zai jagoranci gina katafaren cibiyar musulunci na ƙasa da ƙasa (International Islamic Center) a jihar Kogi

Published

on

FB IMG 16416451298948312
Spread the love

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

Advertisement

Khalifa Muhammadu Sunusi II ya bayyana ƙudurinsa na gina katafaren cibiyar musulunci a jihar Kogi, Khalifa ya bayyana haka ne a jawabinsa na taron maulidi a garin Lokoja, Khalifa yace :

” Tun a jiya wajen cin abincin rana na baiwa gwamnan jihar Kogi takarda na neman izinin mallaka muna fili a jiharsa domin mu gina katafaren cibiyan musulunci na ƙasa da ƙasa, ya cigaba da cewa a da kullum idan muka yi taro irin wannan mukan yi saukokin Alqur’ani ne da addu’oi mu watse ba tare da mu kafa wani abu ba, to yanzu insha Allahu ba zamu rinƙa taro muna watsawa kawai ba sai mun kafa wani abu wanda zai amfani musulmai musamman ‘yan tijjaniyyan dake wurin da ma ƙasa baki ɗaya. Lallai Kogi jiha ce da Allah ya albarkace ta da samun yin suruktaka da maulana Sheikh Sharif Ibrahim Inyass RTA dan haka Kogi jihar Shehu ce.”

Muryar Tijjaniya
✍️ Rayyahi Sani Khalifa
08/01/2022

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *