Connect with us

News

Ganduje Yana Da Laifukan Cin Hanci Da Rashawa Da Yawa Da Zai Amsa – Kwamitin Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa na Buhari

Published

on

FB IMG 1645852404973
Spread the love

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

Advertisement

Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje OFR, wanda yai kaurin suna wajen cusa daloli a aljihu, na fuskantar barazanar tuhuma.

Kwamitin ba shugaban kasa shawara kan yaki da cin hanci da rashawa (PACAC) ya ce gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano yana da tambayoyi da dama dangane da almundahana da zai amsa. Inji Rahoton Daily True Hausa

Sakataren zartarwa na kwamitin, Sadiq Radda ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a dakin taro na yaki da cin hanci da rashawa (ACSR) karo na 26 da aka gudanar a Abuja.

Advertisement

Wasu faifan bidiyo da aka dauko a 2018 a asirce sun nuna Ganduje ya na zuba makudan dalolin amurka. Sai dai ya musanta zargin

Koyaya, a cewar Radda, gwamnan “yana da kararraki da yawa da zai amsa yayin da yake kan mulki da ma fiye da haka bayan ya bar ofis”.

Ya kara da cewa ya yi mamakin yadda dan Ganduje ya kai rahoton mahaifiyarsa ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa bisa zargin zamba.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *