Connect with us

News

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano 

Published

on

FB IMG 1683231314533

A yau Litinin, 4 ga watan Mayu, 2026, an cika shekaru 24 cif da aukuwar mummunan hatsarin jirgin sama a unguwar Gwammaja da ke birnin Kano—ɗaya daga cikin mafi muni a tarihin sufurin jiragen sama a Najeriya.

Hatsarin ya faru ne a ranar 4 ga Mayu, 2002, lokacin da wani jirgi mai ɗauke da tagwayen inji ƙirar BAC 1-11-500, wanda aka ƙera a ƙasar Birtaniya, ya yi hatsari jim kaɗan bayan tashinsa daga filin jirgin sama na Kano, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa jihar Legas.

Advertisement

Dr Umar Ardo Zai Maka Jam’iyyar NDC A Gaban Kotu

Rahotanni sun nuna cewa akalla mutane 148 ne suka rasa rayukansu a hatsarin, yayin da wasu 51 suka jikkata. Daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su har da Ministan Wasanni na wancan lokaci, Ishaya Mark Aku, wanda ke kan hanyarsa ta zuwa Legas domin kallon wasan sada zumunta tsakanin ƙasashen Najeriya da Kenya.

Advertisement

Kamfanin jirgin, EAS Airlines, ya bayyana cewa mutum huɗu ne kawai suka tsira daga hatsarin, ciki har da fasinjoji uku da kuma ma’aikacin jirgin guda ɗaya.

Masana sun bayyana wannan hatsari a matsayin ɗaya daga cikin mafi muni a tarihin jiragen sama a ƙasar nan, sakamakon yawan asarar rayuka da dukiyoyi da ya haifar.

Advertisement

Lamarin ya kuma haifar da ƙara mai da hankali kan tsaurara matakan tsaro da inganta kula da harkokin sufurin jiragen sama a Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending