Connect with us

News

Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji

Published

on

IMG 20260728 150406 618

Shugaban Rundunar Haɗin Gwiwa ta Jihar Kano kan Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi da Safararsu (MATFDAT), Alhaji Muhyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana cewa babu wani mutum ko wata hukuma da za a yi wa rangwame a yaƙin da ake yi da miyagun ƙwayoyi a jihar.

‎Muhyi Magaji ya bayyana hakan ne yayin wani shirin DuniyarMu a Yau, wanda Freedom Radio Kano, inda ya ce duk wanda aka samu yana safarar, sayarwa ko aikata wani laifi da ya shafi miyagun ƙwayoyi zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji

‎Ya ce rundunar ta riga ta kai wasu daga cikin waɗanda suka kamu da shan miyagun ƙwayoyi zuwa Cibiyar Gyaran Hali ta Kiru, domin ba su kulawa da kuma taimaka musu wajen komawa cikin al’umma.

‎Haka kuma, ya bayyana cewa an gurfanar da wasu waɗanda ake zargi da laifukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi a gaban kotu, yayin da aka rufe wasu shagunan sayar da magunguna saboda karya ƙa’idojin da suka shafi sayarwa, adanawa da sarrafa magunguna.

‎“Babu wanda zai tsira. Duk wanda ke sayarwa ko amfani da miyagun ƙwayoyi ba bisa ƙa’ida ba, za a kama shi kuma a gurfanar da shi a gaban kotu. Babu mafaka ga masu aikata irin wannan laifi a Kano,” in ji shi.

Advertisement

‎Shugaban rundunar ya ce za a ƙara faɗaɗa haɗin gwiwa da malaman addini, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin farar hula, ’yan kasuwa, ƙungiyoyin matasa da sauran masu ruwa da tsaki, domin tunkarar matsalar ta hanyar haɗin gwiwa.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending