Connect with us

News

Dakarun Sojin Sun Hallaka’yan Boko Haram Sama Da 50 a Buni Gari A Yobe

Published

on

2026 04 29T123441Z 1896378019 RC2JRHA9SQXX RTRMADP 3 NIGERIA SECURITY

Sojojin Najeriya sun kashe sama da ’yan ta’adda 50 tare da ƙwato makamai da harsasai masu yawa a yankin Buni Gari da ke Jihar Yobe.

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadin Kai (OPHK) ne suka ragarje ’yan bindigar da suka kai hari a hedikwatar Brigade ta 27 da kuma wurin binciken ababen hawa na Buni Gari.

Advertisement

Zaɓen 2027: Dr. Fatah Ya Fitar Da Manufofi Bakwai Domin Inganta Rayuwar Al’ummar Kano Ta Tsakiya ‎

’Yan ta’addan sun kai harin ne da sanyin safiyar Alhamis, lokacin da ’yan ta’addan suka kai farmaki daga wurare daban-daban a cikin duhun dare.

Advertisement

Sanarwar da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar-Kanar Sani Uba, ya fitar, ya ce maharan sun fara kai harin ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare ta ɓangaren yamma, kafin daga bisani su ƙara matsowa ta ɓangaren kudu kusa da Ganinga Junction, sannan suka sake kai wani farmaki ta kudu maso yamma domin mamaye sansanin sojojin.

Sai dai sanarwar ta ce dakarun sun mayar da martani da gagarumin ƙarfin wuta, lamarin da ya haddasa asara mai yawa ga ’yan ta’addan tare da tarwatsa harin da suka kai.

Advertisement

“’Yan ta’addan sun gamu da turjiya mai tsanani yayin da sojojin suka yi amfani da dabarun yaƙi wajen daƙile harin daga dukkan ɓangarorin,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa bayan artabun, dakarun sun ci gaba da bibiyar maharan, inda suka gano gawarwakin wasu daga cikinsu tare da makamai a cikin dazuka da hanyoyin da suka bi wajen tserewa.

Advertisement

Sanarwar ta ce an kuma gano alamun jini a hanyoyin tserewar, wanda ke nuna cewa da dama daga cikin maharan sun samu raunuka masu tsanani.

A cewar rundunar, ko a wani lokaci ba a samu karya garkuwar sansanin sojojin ko wurin binciken ababen hawa ba, domin an ci gaba da riƙe wuraren cikin tsaro har zuwa ƙarshen fafatawar.

Advertisement

Rundunar ta ce ɓangaren sojojin sama na Operation HADIN KAI ya taka muhimmiyar rawa ta hanyar gudanar da aikin leƙen asiri da sa ido, tare da kai hare-haren sama kan wuraren da aka tabbatar ’yan ta’addan sun fake yayin ja da baya.

Hukumomin sojin sun ce hare-haren saman sun kashe karin ’yan ta’adda kusan 20 yayin da jiragen yaƙi ke bibiyar waɗanda suka tsere.

Advertisement

Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigogin AK-47 guda takwas, manyan bindigogi guda biyu, bama-baman RPG guda biyar, na’urorin caji na RPG guda uku, akwatunan harsasai na 7.62mm da wasu karin abubuwan fashewa.

Sojojin sun ce dakarun, tare da haɗin gwiwar jami’an sa-kai, na ci gaba da gudanar da samame domin bibiyar ’yan ta’addan da suka tsere tare da hana su sake haɗuwa.

Advertisement

Sai dai rundunar Operation HADIN KAI ta tabbatar da cewa sojoji biyu sun rasa rayukansu a yayin artabun.

Sanarwar ta yaba da jarumtar sojojin da suka rasu, tana mai cewa sun nuna kishin kasa da sadaukarwa wajen kare Najeriya.

Advertisement

“Dakarunmu sun kasance a kan gaba wajen yaki da ta’addanci, inda suka jajirce domin hana ’yan ta’adda samun damar gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Gabas,” in ji sanarwar.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending