Connect with us

News

Jami’an agaji sun kasa kai wa gamutanen da suka makale a Mariupo

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

Kungiyar agaji ta Red Cross ta ce har yanzu ta kasa shigar da kayan agaji zuwa yankin da aka yi wa kawanya na Mariupol, abin da ya sa ta bukaci bangarori biyun da ke fada – Ukraine da Rasha – da su ba da tabbacin bayar da damar shiga birnin.

Advertisement

Mai magana da yawun kungiyar, Matt Morris ya shaida wa BBC cewa dole a cimma yarjejeniya da bangarorin biyu domin ba da damar kai wa ga dubban mutane da suka makale a birnin da ke tsananin bukatar agaji.

Ya ce hukumar da ke kula da ayyukan jinkai ta duniya na bukatar a bar mutane su bar birnin, kada a turasasa musu.

Advertisement

Ya ce yawancin wadanda ke birnin na zama ne a wuraren fakewa sannan suna fuskantar karantar abinci da ruwan sha dama magunguna.

Ukraine dai na zargin Rasha da tursasa wa dubban fararen-hula komawa wuraren da take iko da su abin da Rasha ta musanta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending